JIHADI PART ONE
kashi na 1
TAQAITACCEN BAYANI AKAN JIHADI
@@@@ @@@@ @@@@ @@@@ @@
بسم الله الرحمن الرحيم
والصلاة والسلام على أشراف أنبياء سيدنا ومولانا محمد النبى وعلى أزواجه أمهات المؤمنين وذريته وأهل البيته الطاهرين وصحابته الأكرمين وعلينا معهم أجمعين
@@@@ @@@@ @@@@ @@@@ @@
Aslm
Ya ‘Yan,uwa Musulmai, Maza Da Mata Manya Da Qanana Ina Fata Muna Cikin Qoshin Lafiya, Marasa Lafiyanmu Allah Ya Ba Su Lafiya Na Gida Dana Asibiti, Mamatanmu Kuma Allah Yaji Qansu Yayi Musu Rahma, In Tamu Tazo Allah Yasa Mu Cika Da Imani.
Ameen Suma Ameen.
.
Yau Cikin Ikon Allah Zamu Dan Rubuta Wani Abu Dangane Da #Jihadi, Daga Littafin Fiqhun Malikiyyah Wato Risala Na Ibnu Abi Zaideen Qirawaniy Rh.
Haqiqanin Gaskiya Wasunmu Basu San /raujimetawiy/ Menene Jihadi Ba, Wasu Sun Dauka Kawai Wani Abu Ne Kamar Ace Rashin Jituwa Ya Shiga Tsakaninka Da Wanda Ba Musulmi, Ka Kashe Shi, Shine Jihadi.
.
A Gurguje
Ga Abunda Malam Abu Muhammada Abdullahi Bin Abi Zaideen Qirawaniy Allah Ya Qara Masa /raujimetawiy/ Yarda Yake Cewa, A Cikin Littafinsa Risala A Babi Na 30 Babu Fil Jihaad.
.
والجهاد فريضة، يحمله بعض الناس عن بعض
Malam Yace : Jihadi Farilla Ne, ( Shi Jihadi Yana Nufin Gwaji,Jarabawa,Gwagwarmaya) Kuma Shi Jihadi Shashin Mutane Suna Daukewa Wasu Shashin, (Kamar Marasa Qarfi, Yara Qanana Haka, Manya Da Jarumai Haka Suna Dauke Musu Yin Jihadi)
.
وأحب إلينا
Mafi Soyuwa A Garemu Shine
أن لا يقاتل العدو حتى يدعوا إلى دين الله
Kada A Yaqi Maqiya Allah Har Sai An Qira Su Izuwa Shiga Addinin Allah (Musulunci) ( Haka Kawai Dan Kuna /raujimetawiy/ Musulmai, Bazaku Fadawa Kafurai Da Yaqi Ba, Dan Kuna Musulmai, Ba Tareda Kun Qira Su Izuwa Shiga Musulunci Ba, Nan In Kun Qira Su Zuwa Musulunci Sunce Baza Su Yi Musulunci Ba, Sannan Ku Musulman Kuce Musu, Toh Tunda Ku Bazaku Musulunta Ba, Toh Ku Bamu Dama Mu isar Da Addinin Allah Izuwa Talakawansu, Daman Da Farko Manyan Gari Kmr Sarakuna Haka Ds, Toh Anan Idan Suka Qi, Suka Ce Basu Musulunta Ba, Kuma Baza Su Bada Daman Isar Da Musulunci Zuwa Talakawansu Ba, Toh Sai Ku Musulmai Ku Ce Toh Shikenan Munji Amma Zaku Dinga Biya Kudin Haraji, Garinku Yana Qarqashin Gwamnatin Musulmai, Toh Anan Idan Su Kafuran Sun Yarda Sunce Zasu Dinga Biyan Kudin Haraji, Qasarsu Sun Yarda Tana Qarqashin Gwamnatin Musulmai, Toh Shikenan Ku Musulmai Baku Da Daman Yaqansu, Sai Ku Barsu.
Amma /raujimetawiy/ Idan Suka Qi Suka Ce Basu Biya Harajin Ba Kuma Qasarsu Bata Qarqashin Gwamnatin Musulunci, Sannan Sunqi Kar6an Musuluncin, Kuma Sunqi Yarda A Isar Dashi Ga Talakawansu, Toh Nan Kam Babu Wata Makawa Za’a Yaqe Su.
Amma Fa Ba Masu Yin Haka, Sai Qasar Da Ginu Da Tsarin Musulunci, Sannan Tsarin Gwamnatacinta Na Musulunci Ne.
Amma Haka Kawai Ana Tsarin Gwamnatacin Turawa, Sannan Ana Zaune Ba Musulmi Ba Kirista Ba Bayahude, Ana Zaune Waje Daya , Zama Zaman Lafiya, Akan Tsarin Gwamnatin Turawa, Sannan Wasu Haka Kawai Su Dauki Makamai, Su Ce /raujimetawiy/ Wai Zasu Yi Jihadi, Toh Wannan Ba Abunda Zasu Yi Illa Ta’addanci.
Allah Ya Qiya She Mu)
إلا أن يعاجلونا
Sai Dai Idan Suka Fado Mana
(Haka Kawai Baza’a Yaqi Kafurai A Take, Sai Idan Haka Kawai Ana Zaune Lafiya, Sai Kafurai Su Fadowa Garin Musulmai Ko Anguwan Musulmai Da Sunan Yaqi, Toh Nan Kam Dole Za’a Yaqe Su, Ko Dan Ma Kare Kai)
.
فإما أن يسلموا أو يؤدوا الجزية وإلا قوتلوا.
Sai Dai Imma Su Musulunta Ko Su Bada Jizya (Haraji) Amma (Idan Aka Je Musu Da Musulnci, Suka Qi Musulunta Suka Qi Bada Haraji, Nan Kam) Za’a Yaqe Su.
( Hikimar Dora Musu Haraji, Shi /raujimetawiy/ Haraji Wata Hikima Ce Kamar Ta Horarwa Ga Kafurai, Ta Yadda Zasu Musulunta, Bawai Cin Zali Bane, Dan Kada Wani Ya Tuhumi Musulunci Da Haka.)
.
وإنما تقبل منهم الجزية إذا كانوا حيث تنالهم أحكامنا
Lalle Ana Qar6an Haraji/Jizya Daga Garesu (Su Kafuran) Idan Sun Kasance (Ko In Garuruwansu Ya Kasance) Hukunce-Hukuncenmu ( Mu Musulmai) Zai Dinga Zuwa Gare Su (Duk Hukunci Da Ake Yanke Zai Je Musu, Toh Shikenan Sai A Qar6i Haraji/Jizyan Tunda Sunce Baza Su Musuluncin Ba.)
فأما إذا بعدوا منا فلا تقبل منهم الجزية
Amma Idan (Kafuran) Suka Yi Nisa Da (Garin) Musulman (Misali Ace Garin Kafuran Yana Cikin Daji Matuqa, Sai An Shiga Daji Sosai, Sai An Wani wuce Koguna Ko Tafki-Tafki, /raujimetawiy/ Ko Sai An Hau Wasu Duwatsu Kafin A Isa Inda Suke) Toh Nan Kam Baza’a Qar6i Haraji/Jiziya Agunsu Ba. (Illa Kawai Ko Su Musulunta Ko A Yaqe Su.)
إلا أن يرتحلوا إلى بلادنا
Sai Dai Idan Sun Yarda Sun Aminta Zasu Na Kawo JizIyan Da Kansu Izuwa Qasan Musulman.
وإلا
In Kuma Ba Haka Ba (Baza Su Musulunta Ba, Kuma Baza Su Kawo Jiziyan Ba.)
قوتلوا
Nan Kam Babu Abun Yi Sai Dai A Yaqe Su.
.
والفرار من العدو من الكبائر
Gudu Daga Wajen Daga Laifi Ne
إذا كانوا مثلى عدد المسلمين فأقل
Idan Adadin/Yawan Kafuran Ya Kasance Kamar Yawan Musulman Ne Dai-Dai Ko Qasa Da Haka. (Toh Gudun Laifi Ne)
فإن كانوا أكثر من ذالك فلا بأس بذلك
Amma Idan Adadin Kafuran Ya Ninka Yawan Musulman Toh Ba Laifii Gudun Don Tsira Da Rai.
.
ويقاتل العدو مع كل بر وفاجر من الولاة
Ana Yaqar Kafurai Daga Shugabanni Tare Da Da’ansa Ko Fajircinsa.
.
Alhamdulillahi Masha Allah
Duka-Duka Anan Zan Tsaya Da Izinin Allah. raujimetawiy
Insha Allahu Zamu Dora A Kashi Na 2 Akan Fadin Mallam RH
ولا بأس بقتل من أسر من الأعلاج
Allah Ya Bamu Ikon Sake Saduwa.
.
Marubuci
#raujimetawiy
#Rabiu_Alhaji_Umar_Jimetawiy
#BPM_PAN_PHM
04 Jimada Sani 1442 Hijra
17 January 2021 Miladiyya
Ranar Lahadi
مع السلام فى أمان الله
https://raujimetawiy.wordpress.com/2021/01/17/jihadi-part-one/
Edited Date And Time
11 Rabi'ul Sani 1446 Hijrah
14 October 2024 Miladiyyah
Comments
Post a Comment